Za mu hada kai da sabbin Shugabannin kananan hukumomi don ciyar da Kano gaba – Gwamna Abba

Date:

Daga Sharifiya Abubakar

 

Gwamnatin jihar kano ta yi alkawarin hada kai da sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomin da Ake zaba domin kawo cigaba jihar Kano.

” Dama Muna yin aiyukan alkhairin yanzu kuma da aka zabi shugabanni za mu tabbatar mun hada kai da su domin kawo aiyukan cigaba a fadin jihar baki daya”.

Talla

Gwamna jihar Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan Jim kadan bayan kada kuri’arsa a zaben shugabannin kananan hukumomin da kansiloli a mazabar Chiranci dake kamar hukumar Gwale .

Ya ce gwamnatin jihar kano karkashin jagorancinsa za ta tabbatar da cewa sabbin Shugabannin kananan hukumomin sun yiwa al’ummarsu aiyukan cigaba.

Zaɓen kananan hukumomi: Kotu a Kano ta sake baiwa KANSIEC sabon umarni

” Waɗannan Yan takarar da ake zaba ko aka zaba sai da aka tsaya aka zabo masu nagarta don haka Ina baiwa al’ummar jihar Kano tabbacin za su yi aiyukan cigaba a dukkanin kananan hukumominsu”. Inji gwamnan

Ya Kuma ba da tabbacin cewa suna da matakai masu yawa da zasu ladabtar da duk wani shugabannin karamar hukumar da aka samu da almundahana da dukiyoyin al’ummarsa.

Talla

Gwamnan ya kuma yabawa al’ummar jihar Kano bisa yadda suka fito domin kada kuri’unsu a zaben shugabannin kananan hukumomin da kansiloli da Ake gudanarwa a dukkanin kananan hukumomi 44 daka jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...