Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

Date:

 

 

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC) ta ce za ta gurfanar da Shugaban Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano (KANSIEC), Farfesa Sani Lawan Malumfashi, tare da Sakataren hukumar, Anas Muhammed Mustapha, da Daraktan Kuɗi na hukumar, Ado Garba, kan zargin wanke fiye da naira biliyan ɗaya.

Za a fara gurfanar da su ne a ranar Litinin, 21 ga watan Yulin 2025, a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

A cewar hukumar ICPC, ana zargin waɗanda ake tuhumar da haɗa baki a tsakanin watan Nuwamba zuwa Disamba na shekarar 2024 wajen aikata almundahanar kudin, wanda hakan ya saba wa dokokin yaƙi da cin hanci.

InShot 20250309 102512486
Talla

Binciken hukumar ya gano cewa an fitar da fiye da naira biliyan ɗaya daga asusun hukumar KANSIEC da ke bankin Unity zuwa kamfanin SLM Agro Global Farm, wanda ba shi da kowace irin alaƙa da hukumar ta KANSIEC.

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Ko da yake wadanda ake zargin sun ce kuɗin anyi amfani dasu wajen biya ma’aikatan wucin gadi da suka yi aikin zabe a nan Kano, sai dai hukumar ICPC ta bayyana cewa wannan bayani ya saba da takardun banki da ƙa’idar kashe kuɗi da aka samu.

Haka kuma an gano wasu kura-kurai a kasafin kuɗin zaɓe, ciki har da naira miliyan 20 da aka ce an kashe wajen tantance ’yan takara a mazabu 484 na Kano, duk da cewa tantancewar ta gudana ne a ofishin hukumar da ke Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...