Tinubu ya buƙaci CAF ta ɗauki mataki kan Libya

Date:

 

 

Shugaban ƙasan Najeriya Bola Tinubu ya yi wa ƴanwasan tawagar Super Eagles maraba da dawowa Najeriya bayan matsalar da suka fuskanta, sannan ya buƙaci a gaggauta bincike, tare da tabbatar da hukunci na adalci game da tirka-tirkar da ta faru da ƴanwasan Super Eagles a Libya.

Tinubu ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai shi shawara na musamman kan harkokin watsa labarai, Bayo Onanuga ya fitar.

Talla

Tinubu ta buƙaci kwamitin ladabtarwa na CAF, “ta yi bincike, sannan ta bayar da shawarwarin irin hukuncin da ya kamata a ɗauka a kan waɗanda suka saɓa ƙa’idoji da dokokin hukumar.”

Da dumi-dumi: Nijeriya ta gayyaci jakadan Libya kan batun Super Eagles

Shugaban ya kuma yaba da ƙoƙarin ma’aikatar harkokin ƙasashen waje da ma’aikatar wasanni bisa ƙoƙarin da suka yi wajen shawo kan lamarin.

Haka kuma ya yaba da juriyar da ƴanwasan suka nuna duk da matsalar da suka fuskanta.

Talla

A ƙarshe ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a harkar ƙwallon ƙafa da su yi duk mai yiwuwa domin hana sake aukuwar irin wannan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hakikanin halin da gwamnan Katsina yake ciki, bayan wani hatsari

  Rahotanni daga Katsina na cewa gwamnan jihar Katsina Dikko...

Zargin almundahana: ICPC ku fita daga harkokin Siyasar Kano – Kungiyar Ma’aikatan KANSIEC

Daga Hafsat Abdullahi Darmanawa   Kungiyar ma'akatan wucin gadi da suka...

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...