Tinubu ya buƙaci CAF ta ɗauki mataki kan Libya

Date:

 

 

Shugaban ƙasan Najeriya Bola Tinubu ya yi wa ƴanwasan tawagar Super Eagles maraba da dawowa Najeriya bayan matsalar da suka fuskanta, sannan ya buƙaci a gaggauta bincike, tare da tabbatar da hukunci na adalci game da tirka-tirkar da ta faru da ƴanwasan Super Eagles a Libya.

Tinubu ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai shi shawara na musamman kan harkokin watsa labarai, Bayo Onanuga ya fitar.

Talla

Tinubu ta buƙaci kwamitin ladabtarwa na CAF, “ta yi bincike, sannan ta bayar da shawarwarin irin hukuncin da ya kamata a ɗauka a kan waɗanda suka saɓa ƙa’idoji da dokokin hukumar.”

Da dumi-dumi: Nijeriya ta gayyaci jakadan Libya kan batun Super Eagles

Shugaban ya kuma yaba da ƙoƙarin ma’aikatar harkokin ƙasashen waje da ma’aikatar wasanni bisa ƙoƙarin da suka yi wajen shawo kan lamarin.

Haka kuma ya yaba da juriyar da ƴanwasan suka nuna duk da matsalar da suka fuskanta.

Talla

A ƙarshe ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a harkar ƙwallon ƙafa da su yi duk mai yiwuwa domin hana sake aukuwar irin wannan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...