Yanzu-yanzu: An sake sassauta dokar hana fita a Kano

Date:

Gwamnatin jihar kano ta amince da sassauta dokar hana fita da aka saka a Kano, inda aka dawo da aka dawo da ta ita daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Dogo Salman ne ya sanar da hakan, bayan ganawar hadin gwiwar majalisar tsaro ta jihar karkashin jagorancin Gwamna Abba Yusuf a gidan gwamnati.

Iyayen matashin da yan sanda su ka harba a Ido a Kano na neman Adalci

Kwamishina Salman ya jaddada kudirin gwamnati na wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar tare da sassauta takunkumin hana jama’a damar ci gaba da harkokin yau da kullum.

Ya kara da cewa matakin sassauta dokar ya nuna yadda tsaro ya inganta da kuma kokarin jami’an tsaro na maido da zaman lafiya a Kano.

Gwamna Yusuf ya kuma bukaci al’ummar jihar da su baiwa jami’an tsaro hadin kai tare da bin ka’idojin dokar hana fita domin tabbatar da ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...