Iyayen matashin da yan sanda su ka harba a Ido a Kano na neman Adalci

Date:

Daga Aminu Halilu Tudun Wada

 

Iyayen wani matashi mai suna Ibrahim Nura Ibrahim wanda ake zargin ’yan sanda sun harbe shi a ido yayin zanga-zangar tsadar rayuwa a Jihar Kano suna neman a bi masa haΖ™Ζ™insa.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito ana zargin yan sanda a Kano da harbin matune, wanda hakan ta sa kungiyoyin kare hakkin dan Adam suke ta kiraye-kirayen a gagguta daukar matakin dakatar da harbin, Sannan gwamnatin jihar kano ta kafa kwamitin bincike don gano wadanda suka yi domin hukuntasu.

A jiya litinin dai gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin kafa kwamitin domin gano yadda akai yan sandan suka harbi mutane da dama a Kano, yayin zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Kano.

Da dumi-dumi: Ƙasar Rasha ta magantu kan Ι—aga tutar ta da Ζ΄an Nijeriya ke yi yayin zanga-zanga

Ibrahim Nura wanda yake mazaunin unguwar Tudun Wada ne da ke karamar hukumar Nasarawa ya ce yan sandan sun harbe shi lokacin da yake kan benen gidansu yana korar yara domin su daina bin yan zanga-zanga a jiya litinin.

A zantawarsa da jaridar kadaura24 Ibrahim ya ce bai ji ba bai gani ba , yan sandan suka harbe shi a ido, wanda hakan ya yi Sanadiyar daina ganinsa bayan an yi masa aiki a idon .

Talla
Talla

” Na ji hayaniyar yan zanga-zangar sun fito daga unguwannin Gama da Tsamiya da Rimin kebe , hakan ta sa na leko ta wundo don hana yara binsu, domin na jiyo wani dan sanda ya na cewa duk wanda ya harba ya harbi banza, kawai Ina tsaye ina yi musu magana sai na ji abu a idona ashe harsashi ne”.

” Ni ban shiga zanga-zanga ba, amma an harbe ni, don haka Ina kira ga gwamnatin jihar kano da sauran kungiyoyin kare hakkin dan Adam da su bi min hakkina Saboda an zalunce ni, ga shi ni maraya ne”. A cewar Ibrahim Nura

Ita ma mahaifiyar matashin ta roki dukkanin masu fada a ji da su taimaka wajen nemawa danta da aka harba ba tare da yayi komai ba hakkinsa.

Idan na fallasa wani sirrin na ka sai jam’iyyarka ma ta kore ka – Kofa ya sake mayar wa Doguwa martani

” Yaron nan ma tun da aka fara Zanga-zangar nan ko wajen baya fita, hasalima da ya ga mun zo zaure ni da kanwarsa haka ya zo yana yi mana fada cewa mu koma gida saboda ka da a biyo yan zanga-zangar ko ayo jifa ko karbi ya sami wani a cikinmu hakan tasa muka koma gida”.

” An ce mu killace ‘ya’yanmu mu hana su shiga zanga-zanga, mun killace su yanzu kuma an zo suna gida ana harbinsu, don haka, Ina kira ga hukumomi da su yiwa Allah su bi mana kadin abun da aka yiwa Ι—ana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related