Za mu Cikawa Daliban Kano Burinsu – Gwamnatin Kano

Date:

Daga Isah Ahmad Getso

 

Mai baiwa gwamnan jihar Kano shawara kan harkokin dalibai Nura Iro ma’aji ya ba da tabbacin gwamnatin Kano za ta yi amfani da shawarwarin da daliban jihar suka bata wajen inganta harkokin ilimi.

” Mun ji korafe-korafe da shawarwarin ku Kuma za mu mikawa gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf domin yin nazari akansu da kuma aiki da su don inganta harkokin ilimi kamar yadda ya faro”

Nura Iron ma’aji ya bayyana hakan ne Yayin taron karbar korafe-korafe da shawarwari daga daliban jihar kano kan yadda za a inganta ilimi, wanda ya gudana a gidan mumbayya House.

Talla

Ya kara da cewa gwamnan kano a shirye yake daya ci gaba da baiwa bangaren ilimin kulawar da ta dace, a kokarinsa na magance dumbin matsalolin da ilimi yake fuskanta a fadin jihar .

Sabbin Sarakunan Rano da Karaye sun ziyarci Sarki Sanusi II

Ya ba da tabbacin gwamnatin jihar kano zata kara bunkasa harkokin zaɓen shugabannin Kungiyoyin dakibai na jihar da na kasa baki daya.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

” Mun fuskanci akwai matsaloli a yadda kuke gudanar da zubukanku , don haka za mu dauki matakan da suka dace don ganin kun shirya sabon zabe, tun da har kun kwashe kimanin Shekaru 8 baku gudanar da zabe ba, wanda kuma hakan ya sabawa dimokaradiyya”.

Daga karshe Yaja hankalin daliban da su maida hankali wajen karatunsu, don cin moriyarsa a nan gaba .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan zaben kananan hukumomin Kano

Kotun ɗaukaka kara dake Abuja, ta rushe hukuncin babbar...

Dole ne yan Nigeria su dage da yawaita addu’o’i a kwanaki 10 Zulhijja – Sheikh Muhd Nasir

Daga Usman Hamza Shugaban majalisar limaman masallatan juma'a na Nigeria...

Mun kama mutanen da mu ke zargi da kashe DPO Rano – Kiyawa

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...

Ku Marawa Tinubu baya don ya ciyar da Kasar gaba – Faizu Alfiindiki ga yan Nigeria

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Jigo a jam’iyyar APC mai mulki,...