Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da fara biyan kudaden tsofaffin kansilolin da suka yi lokacin tsohuwar gwamnatin APC da Kudi sama da Naira Biliyan 16.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’amuran cikin gida na jihar kano Com. Ibrahim Abdullahi waiya ya aikowa kadaura24.

Ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika alƙawarin da ya ɗaukarwa tsofaffin kansilolin da sukai mulki a lokacin gwamnatin Ganduje, na fara biyan haƙƙokin su wanda yace Abdullahi Ganduje ya nuna halin ko in kula dasu lokacin da yake kan mulki.
Kwamishina Waiya ya ƙara da cewa rukunin kansilolin da suka fito daga ƙananan hukumomi 44 daga kuma mazaɓu 484 gaba ɗayan su zasu karɓi haƙƙokin nan ba jimawa ba.
A karan farko dai kansiloli 903 ne suka amfana da naira biliyan ɗaya da miliyan ɗari takwas ₦ 1.8. waɗanda sukai aiki daga shekarar daga 2014 zuwa 2017.
Sai kuma rukuni na biyu da yawansu yakai su yakai 1,198 waɗanda sukai mulki a shekarar 2018 zuwa 2020 kuma zasu karɓi biliyan biyar da miliyan ɗari shida ₦5,6.
Na ƙarshe da sukai a shekarun 2021 zuwa 2024 da yawan su yakai 1,371 da suka zamo kansiloli a wancan lokacin da zasu amfana da biliyan takwas da miliyan ɗari biyu ₦8,2 wanda jimilla yakai biliyan goma sha shida kamar Kamar yadda Sanarwar ta bayyana.