Iftila’i: Gobara ta hallaka ‘yar Kwamishina a Kano, da yan uwansa biyu

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Gobara ta yi sanadiyar hallaka yar Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Kano, Yusuf Kofar-Mata, tare da wasu yan uwansa guda biyu.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a shafin sa na Facebook a ranar Laraba.

Marigayiyar dai ‘yarsa ce mai suna Maimuna, sai yayarsa, Khadija, da matar dan uwansa, Juwairiyya.

Talla

Rahotanni sun bayyana cewa gobara ta kone gidan kwamishinan da ke Kofar-Mata a birnin Kano da safiyar Laraba yayin da iyalan ke barci.

Wata majiyar daga cikin danginsa ta ce gobarar ta lalata wasu kayayyaki masu daraja a gidan.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar, Abdullahi Saminu, ya ce har ba a iya gano adadin barnar da gobarar ta yi ba, da kuma musabbabin tashin gobarar.

A halin da ake ciki, Kofar-Mata ya bayyana alhininsa game da rasuwar yar tasa da wasu ’yan uwansa guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...