Daga Aliyu Danbala Gwarzo
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya yi ikirarin cewa jam’iyyar PDP ce ta ba shi damar karbar mukamin minista a karkashin gwamnatin shugaba Bola Tinubu.
Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas, na cikin ministoci 45 da aka rantsar a hukumance a majalisar ministocin Tinubu a ranar Litinin.

Sai dai nadin na tsohon gwamnan ya janyo suka daga jama’a saboda kasancewar sa a jam’iyyar adawa ta PDP da kuma wata sanarwa da ya yi a baya da ke nuna rashin son zama minista bayan kammala wa’adinsa na gwamna.
A taron manema labarai na farko da ya yi a matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya, Wike, ya ce Tinubu ya rubuta wa gwamnonin jihohi 36, ciki har da na PDP, wadanda a cewarsa, sun ba shugaban kasa sunaye 10 domin ya nada a matsayin ministoci.
Hakikanin Abun da ya faru a Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan Kano a zamanta na ƙarshe
Ya ce: “Ko za ka iya ambata wane ne maƙiyina? Ko za ka iya ambaton mutum guda maƙiyina?” Wike ya ce a taron manema labarai na farko.
“Duba, mutane suna ɗaukar farfaganda. Bari in yi amfani da wannan damar in gaya muku cewa ba na son mutanen da ba sa faɗin gaskiya. Sun ce za su sanya min takunkumi saboda na amince karbi karbi mukamin da aka yi min.
Kawu Sumaila ya ɗauki nauyin Karatun dalibai 100 a Kano ta Kudu
“Shugaban kasa ya rubuta wa gwamnonin jihohi 36 wasikar su kawo sunayen mutane goma da zai basu Muƙami, shin gwamnonin PDP ba su mika sunayen ba? Duk gwamnan PDP ya tura sunayen mutane goma domin a nada su mukami a gwamnatin tarayya .