Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhinin sa kan rasuwar dattijo, fitaccen ɗan kasuwa kuma mai bayar da gudunmawar al’umma, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, wanda ya rasu yana da shekaru 94 a safiyar Asabar, 28 ga Yuni, 2025.

A wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana marigayi Dantata a matsayin jarumin ƙasa da kuma babban rashi ga Najeriya, sakamakon gagarumar gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban tattalin arzikin ƙasar.

InShot 20250309 102512486
Talla

“Alhaji Dantata zai ci gaba da kasancewa cikin tarihin Najeriya saboda kwazonsa, jajircewarsa, da kishin ƙasa da ya nuna ta hanyar sana’o’in kasuwanci da ayyukan jin ƙai da suka shafi rayuwar dimbin ‘yan Najeriya,” in ji Shugaba Tinubu.

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Marigayin ya shahara da basirarsa a harkar kasuwanci, kuma ya taka rawar gani a fagen hidimar jama’a, inda ya taba zama Kwamishinan Tsare-tsare da Ci Gaban Tattalin Arziki a tsohuwar Jihar Kano da sauran muhimman mukaman gwamnati.

Shugaba Tinubu ya kuma ambato irin alaƙar da ke tsakaninsa da marigayin, inda ya bayyana shawarwarin da ya ba shi da goyon bayan da ya nuna masa a matsayin abin karfafa gwiwa da amfani ƙwarai.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Haka kuma, shugaban ya yaba da ayyukan jin ƙai na Alhaji Dantata, musamman a fannonin ilimi da kula da lafiya, wadanda suka taimaka wa rayuwar mutane da dama a fadin ƙasa.

Shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, Gwamnatin Kano da al’ummar jihar bisa wannan babban rashi, yana mai cewa Najeriya ta rasa ɗaya daga cikin fitattun ‘ya’yanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...