Hajjin bana: Wata Hajiya yar jihar Kano ta rasu a Kasar Saudiyya

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano ta tabbatar da rasuwar wata mahajjaciya mai suna Hadiza Isma’il yar asalin karamar hukumar Madobi a kasar Saudiyya.

 

“Hadiza Isma’il daga karamar hukumar Madobi ta rasu a ranar Litinin da misalin karfe 3:15 na rana agogon kasar Saudiyya bayan ta yi fama da gajeruwar rashin lafiya”. A cewar sanarwar

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano ya nada masu bashi shawara na musamman 6, da MD Karota, Radio kano da sauransu

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban tawagar yan jaridun kano a aikin Hajjn bana Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24 .

Talla

Sanarwar ta ce an kai matar mai shekaru 58 a asibitin NAHCON domin jinyar zazzabi kafin a kai ta asibitin Sarki Abdulaziz dake Makka inda aka tabbatar da rasuwarta.

Tuni dai aka binne ta a garin Makka bayan sallar jana’iza a masallacin Ka’aba.

Yadda Jam’iyyar APC ta Gabatar da Shaidu 5 Cikin 300 ga Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Gwamnan Kano

Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano Alhaji Laminu Rabiu Danbappa ya mika ta’aziyyar hukumar ga iyalan mamaciyar a madadin gwamnan jihar Kano, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikanta da rahama ya kuma baiwa iyalai hakurin jure rashin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...