Hajjin bana: Wata Hajiya yar jihar Kano ta rasu a Kasar Saudiyya

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano ta tabbatar da rasuwar wata mahajjaciya mai suna Hadiza Isma’il yar asalin karamar hukumar Madobi a kasar Saudiyya.

 

“Hadiza Isma’il daga karamar hukumar Madobi ta rasu a ranar Litinin da misalin karfe 3:15 na rana agogon kasar Saudiyya bayan ta yi fama da gajeruwar rashin lafiya”. A cewar sanarwar

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano ya nada masu bashi shawara na musamman 6, da MD Karota, Radio kano da sauransu

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban tawagar yan jaridun kano a aikin Hajjn bana Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24 .

Talla

Sanarwar ta ce an kai matar mai shekaru 58 a asibitin NAHCON domin jinyar zazzabi kafin a kai ta asibitin Sarki Abdulaziz dake Makka inda aka tabbatar da rasuwarta.

Tuni dai aka binne ta a garin Makka bayan sallar jana’iza a masallacin Ka’aba.

Yadda Jam’iyyar APC ta Gabatar da Shaidu 5 Cikin 300 ga Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Gwamnan Kano

Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano Alhaji Laminu Rabiu Danbappa ya mika ta’aziyyar hukumar ga iyalan mamaciyar a madadin gwamnan jihar Kano, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikanta da rahama ya kuma baiwa iyalai hakurin jure rashin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...