Hajjin bana: NAHCON ta baiwa jihar Kano gurbin alhazai Sama da dubu 5

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

 

Hukumar Alhazai ta Ƙasa, NAHCON ta baiwa Jihar Kano gurbin alhazai dubu 5902 domin zuwa aikin Hajjin bana, 2023.

 

Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, Muhammad Abba Dambatta ne ya bayyana hakan a yau Asabar yayin ƙaddamar da shirin bita na wannan shekara a Kano.

 

Talla

Alhaji Danbatta ya ce tuni kimanin maniyyata dubu 4 suka biya kudin ajiya.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Danbatta, ya ce gwamnatin jihar ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da ayyukan Hajjin da ke tafe ba tare da tangarda ba.

 

Ya ce hatta aikin Hajjin bara da aka samu matsaloli, jihar Kano ta taka rawar gani inda wanda ya kai ga samun lambobin yabo da dama musamman daga ƙungiya Hajj Reporters.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...