A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin da ake yadawa cewa George Akume ya ajiye aikinsa na Sakataren gwamnatin tarayya.

Kadaura24 ta rawaito A dare ranar asabar ne dai wasu mutane a shafukan sada zumunta suka rika yada cewa Wai George akume ya yi murabus daga mukaminsa na Sakataren gwamnatin tarayya.

InShot 20250309 102512486
Talla

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Kasa Bayo Onanuga ya fitar ya ce labarin na shi da tushe ballantana makama.

Ya ce Shugaban Kasa ba ma ya kasar ballantana a yi Maganar ya sauke wani ko ya nada wani inda ya bukaci al’umma da su yi watsi da labarin ba shi da tushe.

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Sanarwar ta ce babu wani sabon sauyin mukami da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, duk da cewa yana halartar taro a ƙasar Saint Lucia.

Ta ce rahoton da ke yawo game da sauya Akume labari ne na ƙarya da masu tayar da hankali suka kirkira.

Fadar Shugaban Ƙasa ta shawarci ’yan Najeriya da su yi watsi da labaran ƙarya da ake yaɗawa, tana mai jaddada cewa George Akume na ci gaba da kasancewa a matsayin SGF.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...