Nigeria@62: Musa iliyasu kwankwaso ya taya yan Nigeria murna bikin samun yancin kai

Date:

Daga Nura Abubakar

Dan takarar majalisar wakilai na kura madobi da garun Malam Hon. Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso ya taya al’ummar Nigeria dana jihar kano musamman al’ummar Kura Madobi da Garun Mallam.
Musa Iliyasu kwankwanso ya bayyana hakan ne a wani sakon taya murnar cikar Nigeria shekaru 62 da samun yancin kai, wanda ya sanyawa hannu da kansa kuma ya aikowa Kadaura24.
Musa Iliyasu yace ya kamata yan Nigeria su cigaba da hadai kai da kaunar juna don tabbatar da dorewar kasar nan matsayin kasa daya al’umma daya, kamar yadda shugabannin farko irinsu Ahmadu Bello Sardauna da Tarawa Balewa sukai.
Talla
” Nigeria ta hadu da kalubale kala-kala tun daga lokacin da aka bamu yancin kai daga turawa mulkin mallaka, amma abun godiya ga Allah shi ne yadda har yanzu kasar na nan bata tana samun cigaba ta fannoni daban-daban”. Inji Musa Iliyasu
Yace a yanzu da ake da ake tunkarar babban zabe shekara ta 2023 akwai bukatar yan Nigeria su zabi yan takarar jam’iyyar APC domin sune zasu kai kasar nan ga tudun mun tsira.
Talla
” Muna fatan al’umma zasu dubi irin aiyukan alkhairi da jam’iyyar APC ta yiwa al’ummar Nigeria da kuma yadda gwamnatin Dr. Abdullahi Umar Ganduje ta gudanar da aiyukan raya kasa da cigaban al’ummar jihar Kano”. Inji Kwankwanso
Dr. Musa Iliyasu kwankwaso ya kuma bukaci al’ummar jihar Kano da kasa baki daya da su cigaba da yiwa shugabanni addu’a don su sami damar cigaba da yiwa al’umma aiki da kuma cigaba da hada kan kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...

Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Masarautar Gidan Igwai ta dakatar da Usman Umar wanda...

Masu yada hotunan Akpabio a ofishin SDP suna yi ne don bata sunan Jam’iyyar – Hon. Ali Shattima

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban Jam'iyyar SDP na jihar Kano...