Gwamnatin jihar kano ta hana makarantar Kano Capital karin kudin makaranta ga dalibanta

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

 

Ma’aikatar Ilimi ta jihar Kano ta umarci hukumar gudanarwa ta makarantar Kano Capital data janye sabon karin kudin makaranta data yi.

 

Babbar sakatariya a ma’aikatar Hajiya Lauratu Ado Diso ce ta bayar da wannan umarni yayin da take kaddamar da kwamitin da zai yi nazari kan rahotannin makarantar na baya da aka gabatarwa ma’aikatar domin aiwatarwa.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kai na ma’aikatar Ilimi Aliyu Yusuf ya sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24 a ranar juma’a.

 

Babbar sakatariyar ta tabbatarwa iyayen Daliban da abun ya shafa cewar ma’aikatar zata tabbatar komin an dorashi kan gurbinsa, ta hanyar amfani da ka’idoji da kuma doka, inda ta bukace su dasu kwantar da hankalinsu sannan kuma su kasance masu bin doka.

 

Ta kara da cewa an kafa kwamitin ne domin yin nazari kan rahotanni baya na makarantar da aka gabatar masu game da wasu matsaloli da aka gano a makarantar domin aiwatarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya...

Aiyuka 5 da Gwamnan Kano ya yi alkawarin yi, bayan dakatar da rusau a Rimin Zakara

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci garin Rimin Zakara...

Shugaban K/H Garun Mallam zai Raba Audugar Mata 500 ga Makarantun Sakandiren Matan yankin

Daga Safiyanu Dantala Jobawa Shugaban karamar hukumar garun mallam Aminu...

Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...