Ni ginshiki ne a PDP idan na bar ta mutuwa za ta yi– Kwankwaso

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa
 Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Kwankwaso, yace yana da yakinin cewa jam’iyyar PDP za ta rushe da zar ya fita daga cikin jam’iyyar.
Kadaura24 ta rawaito Kwankwaso duk da cewa a halin yanzu baya jin dadin  jam’iyyar,Amma ya bada tabbacin har yanzu yana Cikin jam’iyyar Bai Kai ga fita ba.
 Ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a wani shirin gidan Talabijin na Channels, a cikin shirin  Political Paradigm.
 Kwankwaso ya yi tsokaci kan wasu dalilan da suka bayan jin dadin yadda ake tafi da jam’iyyar PDP, inda ya ba da misali da abun da faru a taron shiyyar Arewa maso Yamma da aka yi kwanan nan a Kaduna.
 “Ya kamata in kasance daya daga cikin masu fada a ji a jam’iyya PDP,” Amma ana ganin ban Isa ba Kuma Wasu Suna raina matsayina a jam’iyyar wanda ni Kuma bazan lamunci irin wannan wulakancin ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Tinubu

  Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya...

Yanzu-yanzu: Jam’iyyar APC ta yi Sabon Shugabanta na Kasa

  Ministan Jinkai da ba da Agajin Gaggawa, Farfesa Nentawe...

Ku shiga harkokin Kasuwanci domin akwai albarka a ciki – Sarkin Kabin Jega ga matasa

Daga: Ibrahim Sidi Mohammad Jega Sarkin Kabin Jega, Alhaji Muhammad...

Kotua a Kano ta yankewa G-Fresh hukuncin zaman gidan yari

Kotu ta aike daAbubakar Ibrahim G. Fresh gidan gyaran...