Alhaji Munzali Sani Musa ya zaman sabon Uban kungiyar yan Kasuwar Kano

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Hadaddiyar Kungiyar yan Kasuwar jihar kano ta nada Alhaji Munzali Sani Musa a matsayin uban kungiyar bayan rasuwar marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata Wanda ya kasance shine uban kungiyar a lokacin da yake Raye.

Shugaban kungiyar Alhaji Auwalu Jakada Gabari yace sun zabi Alhaji Munzali Sani Musa ne bisa la’akari da yadda ya ke tallafawa harkokin kasuwanci da yan kasuwa manya da kuma kanana a bangarori da dama, wanda hakanne ta sa suka bashi wannan matsayi domin samun damar cigaba da yiwa al’umma hidima.

InShot 20250309 102512486
Talla

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya Kadaura24 t rawaito hadaddiyar Kungiyar ta bayyana Alhaji Kabiru Sani Kwangila Yakasai Khadimun Nabiyyi a matsayin uban kungiyar inda daga bisani ya ajiye mukamin bisa radin kansa.

Shi dai Alhaji Munzali Sani Musa ya kasance babban Dan kasuwa wanda yake gudanarda harkokin kasuwancinsa a ciki da wajan kasarnan, wanda kuma Aminine ga Alhaji Kabiru Sani Kwangila yakasai SKY khadimun Nabiyyi .

Da dumi-dumi: NNPC ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Da yake jawabi Alhaji Munzali Sani Musa ya ce wannan matsayi da aka dora masa, ba nasa shi ba ne shi kadai, kuma ya Sha alwashin aikin aiki tukuru bisa Gaskiya da adakci don cigaban Kasuwanci a jihar kano .

Ya kuma bukaci sauran mawadata dake jihar kano dasu hada kai domin kara inganta harkokin kasuwanci da tallafawa yan kasuwa a matakai daban daban

Taron ya gudana a farfajiyar gidan Alhaji munzali sani musa dake rukunun gidajen Nasarawa dake lugard.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...