Yakin Ukraine: Amurka ta gargadi China Kan kawancenta da Rasha

Date:

Amurka ta ce ta yi gargaɗi ga China cewa babu wata ƙasa da za sha a koƙarinta na ceto ƙasar Rasha daga halin da ta shiga na takunkuman da aka ƙaƙaba mata kan hare-haren da ta ke kai wa a Ukraine.

Mai ba da shawara kan sha’anin tsaro na amurka Jake Sullivan ya ɗauko batun kai-tsaye inda ya bayyana damuwarsa a lokacin da yake tattaunawa da jami’in diflomasiyyar China Yang Jiechi, a birnin Rome na Italiya.

Ya ce Amurka tana kallon ta inda China za ta taimakawa Putin.

Kafin tattaunawar a Rome, Jami’an Amurka sun ce Rasha har ta nemi taimakon soji ga China. Gwamnatin China kuma ta bayyana ikirarin na Amurka a matsayin labarin kanzon kurege.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...