Kungiyar Kwadago ta yi Watsi da Batun Karin Kudin Man Fetur

Date:

Kungiyar Kwadago ta kasa NLC, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yin watsi da shirin kara farashin man fetur a Nigeria.
 Shugaban Kungiyar, Kwamared Ayuba Wabba ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja.
 A cewarsa, Manajan Darakta na Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPC), Malam Mele Kyari, ya sanar da cewa man fetur zai iya tsada har N340 daga watan Fabrairun 2022.
 Solacebase ta rahoto cewa Wabba ya bayyana Matakin da Gwamnatin tarayya ta dauka na cewa gwamnati zata Rika baiwab ‘yan Najeriya miliyan 40 Naira 5,000 a matsayin abin da zai magance illar karuwar farashin man fetur.
 Ya ce jimillar kudaden da suka ce zasu Rika baiwa Yan Kasa ya zarce kudaden da gwamnati ta ce tana kashewa a halin yanzu kan tallafin man fetur.
 Shugaban NLC ya ce duk wani yunkuri na kwatanta farashin man fetur a Najeriya da sauran kasashen duniya zai Zama kuskure ne domin Kamar ka kwatanta tuffa da mangwaro ne

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...