NNPC ta ce Yan Nigeria Zasu Sayi Litar Man Fetur Naira 320 Zuwa 340 a Shekara Mai Zuwa

Date:

Kasa da mako guda bayan da Hukumar Bada Lamuni ta Duniya ta baiwa gwamnatin Najeriya shawarar cire tallafin man fetur domin karkata kudaden da take zubawa zuwa ayyukan raya kasa, shugaban kamfanin man NNPC Mele Kyari yace farashin man na iya kaiwa naira N320 zuwa N340 kowanne lita daga shekara mai zuwa.

Yayin da yake gabatar da jawabi a Abuja, Kyari yace tabbas babu abinda zai hana cire tallafin man a shekara mai zuwa, domin kuwa dokar da ake amfani da ita wajen biyan tallafin zata daina aiki daga karshen watan Fabarairu mai zuwa.
Shugaban kamfanin man yace a shekara mai zuwa babu wani tanadi da akayi na sanya kudin tallafin, kuma ganin yadda ayyuka suka yiwa gwamnati yawa, zasu aiwatar da shirin janye shi a cikin sauki.
Dangane da tashin farashin iskar gas da ake girki da shi kuwa, Kyari yace batu ne na karuwar bukatar sa ta haifar da hauhawan farashin tare da karancin sa a kasuwannin duniya.
Shugaban kamfanin NNPC yace dama iskar gas bashi da wani tallafin da gwamnati take sanyawa, saboda haka farashin sa na tafiya ne da yadda kasuwar duniya take a koda yaushe.
RFI ta rawaito Kyari ya bayyana cewar kamfanin NNPC na iya bakin kokarin sa wajen kara yawan iskar gas din da ake sayarwa a cikin gida domin biyan bukatar masu aiki da shi.
Ita kuwa ministar kudi, Zainab Ahmed cewa tayi gwamnati zata cire tallafin domin baiwa ‘Yan Najeriya matalauta naira N5,000 kowanne wata a matsayin tallafin sufuri.
Ministar tace akalla ‘Yan Najeriya miliyan 30 zuwa 40 ake saran su ci gajiyar shirin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...