Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Date:

Daga Aminu Gama

 

Kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a fagge yan alluna a jihar Kano ta aike wani magidanci da ake zargi da ikirarin bin mamata bashi zuwa gidan gyaran hali.

Mai shari’ar Umar lawan Abubakar na kotu mai lamba 1 a unguwar fagge yan Alluna ne ya bayar da umarnin garkame mutumin har zuwa ranar 14 ga watan 04 2025 domin cigaba da sauraren karar.

Tun da farko lauyan Gwamnati Zaharaddini Mustapha ne ya karantawa wanda ake kara tuhumar da ake yi masa.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ana dai tuhumar mutumin ne da zargin zuwa gidajen da aka yi mutuwa inda yake karyar cewa yana bin wanda ta rasu kudi.

An dai kama mutumin ne yayin da ya je gidan su wani mamacin mai suna Yusuf Mansur Ashura inda ya yi da’awar yana bin mamacin kudi Naira dubu dari uku sakamakon kasuwancin Doya da suka yi.

Sai dai da aka zurfafa bincike sai aka gano mutumin karya yake yi, saboda an sami akalla mutane uku a gidan mutuwar da suka ce sun gane shi, domin mutumin ya taba zuwa ya ce yana bin mamatansu kudade.

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga nan ne aka mika shi ofishinsa yansanda inda su kuma suna kawo shi kotu don ya girbi abun da ya shuka.

Tuni dai wanda ake kara ya amsa laifinsa kuma ya roki mai shari’ar da yayi masa sassauci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...