Yanzu-Yanzu : IG ya dakatar da Abba Kyari kan zargin Rashawar miliyoyin daloli na Hushpuppi

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nigeria Usman Alkali Baba, ya amince da dakatar da DCP Abba Kyari daga Rundunar ‘Yan sandan Najeriya har zuwa lokacin da sakamakon binciken da ake Yi akansa Zai kammala.

Kadaura24 ta rawaito Cikin Wata wasika mai dauke da kwanan wata 31 ga Yuli, 2021, ya amince da shawarar dakatar da jami’in, Inda yace hakan ya yi daidai da matakan ladabtarwa na rundunar.

Cikin Wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar Frank Mba ya fitar a safiyar Ranar Lahadi nan yace IGP ya kara da cewa dakatarwar ana kuma sa ran zata samar da yanayi mai kyau ga kwamitin bincike na musamman na Rundunar don gudanar da bincike kan manyan zarge -zargen da ake yiwa DCP Abba Kyari ba tare da tsangwama ba.

Kwamitin Binciken na Musamman (SIP), wanda ya kunshi Manyan Jami’an ‘Yan Sanda guda hudu (4), yana karkashin jagorancin DIG Joseph Egbunike, Mataimakin Babban Sufeto Janar na‘ yan sandan da ke kula da sashin binciken manyan laifuka (FCID). Hukumar ta SIP, Kwamitin Binciken zai gudanar da cikakken nazari kan dukkan zarge -zargen da gwamnatin Amurka ke yiwa DCP Abba Kyari kamar yadda yake kunshe cikin takardun da suka dace da hukumar binciken manyan laifuka ta tarayya (FBI).

Sanarwar tace Kwamitin din kuma zai sami cikakken wakilcin DCP Abba Kyari ga dukkan zarge -zargen da ake yi masa, da gudanar da bincike kamar yadda ya dace, da kuma gabatar da shawarwari don jagorantar karin ayyukan da Jagorancin Rundunar a kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...