Yanzu-Yanzu :Yan Sanda a Zamfara sun kubutar da Dalibai 2 Cikin Daliban da aka sace a Yauri

Date:

Daga AB Kaura

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ceto dalibai biyu daga cikin daliban da aka sace na kwalejin Birnin Yauri a jihar Kebbi.

Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan ‘yan sanda na rundunar,CP Hussaini Rabiu ya baiyana haka yayin ganawarsa da manema labarai a hedikwatar’ yan sanda da ke Gusau ya ce an ceto daliban ne a kauyen Babbar Doka da ke gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru a jihar Zamfara.

“Ma’aikatan mu na Operation zaman lafiya sun yi nasarar kubutar da dalibai biyu wato Maryam Abdulkareem ‘yar shekara 15 a karamar hukumar Wishishi ta jihar Neja da Faruk Buhari dan shekara 17 na karamar hukumar Wara ta jihar Kebbi lafiya a Kauyen Doka a gundumar Dansadau ”inji CP Hussaini .

Kwamishinan ya yi bayanin cewa, an kai daliban asibiti domin duba lafiyarsu kuma ‘yan sanda suna kara samun bayanai Daga Daliban.

Lura da cewa, za a mika daliban ga rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi don ci gaba da daukar matakan da suka dace tare da mika su ga Iyayen su.

Wasu daga Cikin yan uwan daliban da aka sako wadanda suka halarci taron manema labaran sun nuna farin ciki tare da nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Kuma kokarin ‘Yan Sandan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...