Mutane uku sun Jikkata sakamakon gobara a shagon siyar da Gas a Hotoro

Date:

Daga Sani Magaji Garko

Al’ummar Layin Garsan Fulani cikin Unguwar Hotoron Arewa a Karamar hukumar Nasarawa da ke nan Kano sun shiga cikin dimuwa sakamakon tashin Gora a shagon siyar da Gas.

Wani da abin ya faru a idon sa Malam Abdullahi ya bayyana wa manema labarai cewa wutar ta tashi ne sakamakon kan tukunyar gas ya da ki keken dinki.

Lamarin ya shigar da mautanen yankin cikin tsoro Wanda hakan ya sa makotan shagon guduwa daga gidajen su domin neman mafaka.

Wani shaidar gani da ido ya ce mutane uku sun sami raunuka ciki harda wata matar Aure dake makwabtaka da shagon, yayin da wutar ta tarwatsa masu kade-kaden bukukuwan aure a kusa da abin da ya faru.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin.

Saminu Yusif Abdullahi ya ce sun sami Kira daga wani Malam Anas Musa da misalin karfe 8:52 cewa wani shagon siyar da Gas ya kama da wuta a Hotoro tsamiyar Boka layin Garsan Fulani.

Kadaura24 ta rawaito cewa Saminu Yusuf ya ce suna samun lamarin suka yi gaggawar tura jami’an su inda cikin kankanin lokaci suka shawo kan matsalar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...