Usman bin Zubair ya lashe zaben fidda gwani na dan Majalisar jiha a Gwale

Date:

Daga Ibrahim Abubakar Diso

Usman Bin Zubair ya lashe zaben fidda gwani na Dan Majalisar dokokin Jihar kano cikin jam’iyyar APC daga Karamar Hukumar Gwale.

Baturen zaben fitar da gwani na majalisar dokoki ta jihar kano a karkashin jam’iyyar APC a karamar hukumar Gwale Alhaji Danlami Zakari unguwar gyattai ya sanar da cewa Usman Bin Zubair ya lashe zaben kuri’u Masu yawa.

Alh Danlami Zakari ya bayyana hakan ne jim kadan da kammala jefa kuru ‘u da dalagate sukai a ofishin hisba dake Gwale, yace Usman Bin Zubair ya sami kuru’u arbain da shida 46 cikin hamsin da aka jefa .

An dai gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali , sannan Alh. Danlami Zakari ya yabawa mahukuntan jam’iyya APC da Jami’an tsaro bisa gudunmawar da suka bayar har zaben ya gudana cikin kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...