Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I Jibrin, ya kammala shirye-shiryen bayar da tallafin karatu ga dalibai 1,000 don yin karatun digiri a fannonin da suka shafi fasahar zamani, ICT, ƙarƙashin Gidauniyar Barau I Jibrin, BIJF.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai taimakawa Sanatan kan harkokin yada labarai Ismael Muddashi .

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar ta ce wadanda za su ci gajiyar shirin su ne daliban da su ka fara karatu a cibiyoyin karatu guda bakwai a Jami’ar Tarayya da ke Dutsin-ma da ke Jihar Katsina da za a kafa a mazabar Kano ta tsakiya da ta Kudu daga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa.

Ya ce Sanata Barau da mahukuntan jami’ar sun kammala shirye-shiryen kafa cibiyoyin karatu a mazabun biyu.

Matasan da Barau Jibrin ya dauki nauyin karantunsu sun bar Kano zuwa India

Sanata Barau Jibrin ya dauki wannan matakin ne a kokarinsa na tallafawa matasa Maza da mata don inganta rayuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...