Musa Iliyasu Kwankwaso ya zama dan takarar Majalisar Kura Madobi da Garum mallam a APC

Date:

Daga Safyanu Dantala Jobawa

Tsohon kwamishinan raya karkara na jihar kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya lashen zaben fidda gwani na takarar dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kura/Madobi/Garun mallam.

 

Yayin zaben Musa Kwankwaso ya lashe zaben ne da kuru’u 150, yayin Dan Majalisa Mai Wakiltar yankin Hon Kabiru Danhassan ya sami kuru’u 4, sai kuma Hajiya Hama Ali Aware Garun mallam ta sami 6.

Musa Iliyasu Kwankwaso dai tsohon Kwamishinan Ma’aikatar raya karkara ne a zamanin mulkin Malam Ibrahim Shekarau da Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

 

Yanzu dai Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso shi ne zai wakilci jam’iyyar APC a Babban zabe Mai zuwa na shekarar 2023, Inda ake ganin Zai iya yin nasara Saboda farin jinin da yake da shi a wurin al’ummar yankin Kura Madobi da Garum mallam.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...