Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

Date:

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA’IB)

Assalamu Alaikum Warahmatullah,

Sakamakon rasuwa da Allah ya yiwa Alhaji Aminu Alhassan Dantata a Hadaddiyar Daular Larabawa a jiya Juma’a, Majalisar Malamai ta Kasa reshen Jihar Kano tana gayyatar daukacin al’umma domin halartar Sallatul Ga’ib na addu’ar rahama ga mamacin.

InShot 20250309 102512486
Talla

Za a gudanar da Sallatul Ga’ib din a yau, Asabar 28/06/2025, a Masallacin Umar Bin Khattab, dake Dangi, Kano, da misalin karfe 2:00 na rana.

Ana rokon al’umma da su hallarci wannan ibada domin neman rahamar Allah ga mamacin, tare da yi masa addu’ar samun gafara da jinƙai.

Allah ya jikansa, ya sanya Aljannah makomarsa.

Wassalamu Alaikum Warahmatullah.

Sanarwa:
Salisu Umar Gama,
A madadin Shugaban Majalisar Malamai,
Malam Ibrahim Khalil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...