Fadan daba ya sa an hade Sallar Magariba da Isha’i a wata unguwa Kano

Date:

Daga Munnira Ahmad

Al’ummar unguwar Dorayi dake karamar hukumar Gwale a jihar Kano sun koka da yadda fadan daba ke kara tu’azzara a yankin wanda har ya tisalta musu hade Sallar magariba da isha’i a jiya lahadi .

Wani mazaunin yankin da Jaridar Kadaura24 ta zanta da shi bisa Sharadin boge sunansa, ya ce a jiya lahadi fadan daba ya tilastawa wasu masallatan yankin Dorayi Karama, zuwa konannen gidan mai da Karshen waya hade Sallar magariba da ta Isha’i.

IMG 20250415 WA0003
Talla

” Lamarin fadan daba ya Zama abun da ya Zama domin wasu masallatan akan idona suka rika hade Sallar Magariba da Isha saboda yadda yaran suke cin karensu babu babbaka a yankin mu, kuma har yanzu an ki a dauki wani mataki da zai magance matsalar”. Inji shi

Ya ce fargaba da firgice ne suka tilastawa mutane daukar Wannan matakin na hade wadannan salloli.

Fadan daba: An yi wa wani matashi yankan Rago a Gayawa

Sai dai majiyar ta mu ta shaida mana cewa limamin masallacin almuntada dake unguwar ta Dorayi Sheikh Aminu Library ya ce shi ba zai hade Sallar Magariba da isha’i ba saboda fadan daba.

Inda ya ce wajibi ne mutane su Kare kawunansu tunda hukumomin da Lamarin ya shafa sun gaza magance matsalar da ya jima tana ci wa al’ummar yankin tuwo a kwarya .

InShot 20250309 102403344

Ya bukaci mahukunta da su tashi tsaye domin sauke nauyin da Allah ya dora musu na Kare rayuka da dukiyoyin al’ummar da suka zabe su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...