Jan fentin da aka sanya a Rimin Zakara ba na rusau ba ne, na kawo cigaban gwamnna ne – Nazifi Tijjani

Date:

Daga Nazifi Dukawa

 

Shugaban Kungiyar masu siyar da filaye, gidaje da kangwaye kuma mai kamfanin Annatija Properties Alhaji Naziru Tijjani Idiris ya karyata labarin rusau a garin rimin zakara da wani yayi zargi.

Alh Naziru Tijjani Annatija ya ce sanya Jan fenti alkhairi ne ya zo garin gwamnnatin jihar kano ce ta zo da karin cigaba a garin don cigaban da farantawa al’ummar yankin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ya ce waccen maganar ta tunani za a sake yin rusau a gari babu kamshin gaskiya a cikinta .

“Idan za a yi rusau ana rubuta alamar rushewa , Amma wanan kuma alama ce ta kidaya gidajen da kangwaye ce domin cigaban da tallafawa mazauna yankin”. Inji Naziru Tijjani

Al’ummar Rimin Zakara sun musanta zargin sake yin Rusau a garin, sun kori wanda ya yi zargin

Alhaji Naziru Tijjani Annatija ya ce idan mutane za su iya tunawa a baya gwamnan ya yi alkawarin kawo wutar lantarki yankin da asibiti da makaranta har ma da masallacin Juma’a.

InShot 20250309 102403344

“A halin yanzu kullum ma’aikatan gwamnnatin su na zuwa yankin don cigban da kawo ayyukan alkhairi a yankin don haka masu gidaje da filaye da kangwaye su kwantar da hankalinsu babu abun da zai faru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...