Sarkin Musulmi ya umarci yan Nigeria su fara duban watan Zulhijja

Date:

Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ta bukaci al’ummar Musulmin Nigeria da su fara duban jinjirin watan Zulhijja na shekara ta 1446.

 

“Gobe talata 27 ga watan mayun 2025, ita ce daidai da 29 ga watan Zulqida shekara ta 1446 don haka ita ce ranar da za a fara duban jinjirin watan Zulhijja na bana”.

Yadda Rikici ya barke tsakanin yansanda da mutanen gari a Kano

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci na fadar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Sanarwar duk wanda ya ga watan ya sanar da wani basarake mafi kusa da shi domin mika sanarwar ga fadar mai alfarma Sarkin Musulmi domin tantancewa.

Kadaura24 ta watan Zulhijja dai shi ne wata na karshe a kalandar addinin musulunci, kuma a watan ne al’ummar Musulmi suke zuwa garin Makka domin gudanar da Ibadar aikin Hajji

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...