Gobarar Kwalema: Atiku Abubakar ya jajantawa Matawallen Gwagwarwa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya bukaci gwamnatin jihar Kano da gaggauta tallafawa mutane da iftila’in gobarar Kwalema ta shafa don inganta rayuwarsu.

“Ina kira ga gwamnan jihar Kano da ya gaggauta fara gudanar da cikakken bincike kan musabbabin faruwar wannan gobara domin hana afkuwar irin wannan a gaba. Bugu da ƙari, ina kira ga gwamnati da ta ba da agajin gaggawa da tallafi ga wadanda abin ya shafa tare da aiwatar da matakan dakile sake faruwa a nan gaba”.

InShot 20250309 102403344
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya wallafa a sashin shafinsa na Facebook da safiyar ranar alhamis din nan.

“Na yi matukar bakin ciki da yadda wata gobara ta tashi a wata karamar masana’anta da ake sarrafa kayayyaki da kasuwanci da ke unguwar Dakata a Jihar Kano da safiyar ranar Larabar da ta gabata”.

Iftila’i: Gobara ta Kone Kasuwar Yan Gwan-Gwan da ke Kano

Ina addu’ar duk wadanda suka rasa dukiyoyinsu da rayuwarsu a wannan lamari mai cike da takaici Allah ya mayar musu, Tabbas an yi asarar biliyoyin nairori, wannan babban rashi ne, ba wai ga wadanda abin ya shafa ba, har ma ga daukacin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hawan Sallah: Yansandan Kano sun gayyaci hadimin Sarki Sanusi II bayan mutuwar wani

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...

Barka da Sallah: Gwamnan Kano ya bukaci yan jihar su rungumi zaman lafiya da adalci

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Sarki Aminu da Sarki Sanusi sun bukaci gwamnati ta hukunta duk masu hannu a kisan Mafarautan Kano a Edo

Daga Aliyu Danbala Gwarzo da Sani Idris maiwaya   Mai Martaba...

Murtala Sule Garo ya yiwa Kanawa Barka da Sallah

Ina taya daukacin al’ummar Musulmi maza da mata musamman...