Gwamnan Kano ya nada mataimakin mai magana da yawunsa da wasu mukamai

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nada wasu mukamai da karin girma a wani yunkuri na karfafa harkokin mulki da inganta ayyuka a gwamnatinsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

Wadanda aka nada ko kuma aka karawa mukamai daban-daban sune kamar haka.

InShot 20250309 102403344
Talla

1- An nada Architect Hauwa Hassan Tudun a matsayin Manajan Darakta ta Hukumar Tsara Burane ta Kano (KNUPDA)

2- An nada Mustapha Muhammad a matsayin babban sakataren yada labarai na gwamna kuma mataimakin kakakin mai magana da yawun gwamnatin Kano Sunusi Bature D/Tofa

3- An nada Auwal Lawan Aramposu a matsayin mataimakin Manajan Darakta na Hukumar KAROTA.

4- An nada Dr. Tukur Dayyabu Minjibir a matsayin mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin noma.

Baya ga wadannan muhimman mukamai, Gwamna Yusuf ya amince da karin girma ga wasu manyan jami’ai guda biyu.

Gwamnan Kano ya Bayyana Matsayarsa Game da Hawan Sallah Karama a Jihar

1- Zulaihat Yusuf Aji ta samu mukamin mataimakiyar Manajan Darakta ta gidan radiyon jihar Kano.

2- Injiniya Abduljabbar Nanono ya zama mataimakin Manajan Darakta na KHEDCO.

A yayin da yake taya sabbin wadanda ya nada Murna, gwamnan Kano ya ba su tabbacin goyon bayansa, sannan ya bukace su da su yi aiki tukuru a kan ayyukansu domin bayar da ta su gudummawar don ci gaban jihar Kano

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...