Masu yada hotunan Akpabio a ofishin SDP suna yi ne don bata sunan Jam’iyyar – Hon. Ali Shattima

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Shugaban Jam’iyyar SDP na jihar Kano Hon. Ali Shattima Tudun Murtala ya musanta labarin dake yawo a shafukan sada zumunta cewa shugabannin majalisar dattawan Nigeria sun Kai wata ziyara ofishin Jam’iyyar ta su.

” Yadda ku ka ga Wannan hotunan nima haka na gansu, amma abun da suke yadawa karya ce , domin tsohon hoto ne da aka dauke shi kusan sama da shekara guda data gabata”.

InShot 20250115 195118875
Talla

Hon. Ali Shattima ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa ta musamman da yayi da jaridar Kadaura24 ranar lahadi.

 

” An dauki hoton ne lokacin da Shugabannin majalisar Sanata Godswil Akpabio da Barau Jibrin suka ziyarci ofishin Jam’iyyar SDP kamar yadda suka ziyarci na jam’iyyun PDP da LP da NNPP domin neman goyon bayan sanatocin jam’iyyun kafin su zama Shugabannin majalisar”. Inji Hon. Ali Shattima

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Ya ce masu yada tsofaffin hotunan suna yin haka ne saboda sun ga yadda jam’iyyar SDP ta yunkuro domin ta karbi kasar nan.

Hon. Ali Shattima Tudun Murtala ya bukaci al’ummar Nigeria da su yi watsi da masu yada wadancan hotuna saboda suna yi ne kawai don bata Jam’iyyar SDP a wajen al’ummar Nigeria

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...