Nasiru Ja’o’ji ya ziyarci mataimakin shugaban Kasa, Kashim Shettima

Date:

 

 

Hon. Nasiru Bala Aminu Ja’o’ji ya ziyarci mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima.

Ja’o’ji ya ziyarci mataimakin shugaban kasar ne a gidansa da ke fadar gwamnatin tarayya a Abuja.

A lokacin ziyarar sun tattauna abubuwa masu mahimmanci da su ka hada da ci-gaban jam’iyyar APC da na matasa a jihar Kano da kuma Arewacin Najeriya gaba daya.

InShot 20250115 195118875
Talla

Shettima ya yabawa Ja’o’ji bisa irin gudunmawar da ya ke baiwa jam’iyyar APC a jihar Kano da kuma Arewacin Najeriya.

Shettima ya ce tabbas jam’iyyar na alfahari da matasa irinsu Ja’o’iji wadanda ke aiki tukuru dan bunkasa jam’iyyar.

Haka zalika Shettima ya ce jam’iyyar na sane da irin kabakin alkairi da Ja’o’ji ke yiwa matasa da mata a jihar Kano.

Kwamishina a Kano ya mayar da rarar Naira Miliyan 100 Asusun Gwamnati

A lokacin da ya ke bayani, Ja’oji ya godewa mataimakin shugaban kasar kan tarbar da ya yi masa.

Ya kuma yi alkawarin ninka gudunmawar da ya ke bawa jam’iyyar ta hanyar bada tallafi ga matasa da mata kamar yadda ya saba.

A watan Disamba shekarar da ta gabata Ja’o’ji ya bawa matasa da mata tallafin miliyan 500 don su dogara da kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...