Nasiru Ja’o’ji ya ziyarci mataimakin shugaban Kasa, Kashim Shettima

Date:

 

 

Hon. Nasiru Bala Aminu Ja’o’ji ya ziyarci mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima.

Ja’o’ji ya ziyarci mataimakin shugaban kasar ne a gidansa da ke fadar gwamnatin tarayya a Abuja.

A lokacin ziyarar sun tattauna abubuwa masu mahimmanci da su ka hada da ci-gaban jam’iyyar APC da na matasa a jihar Kano da kuma Arewacin Najeriya gaba daya.

InShot 20250115 195118875
Talla

Shettima ya yabawa Ja’o’ji bisa irin gudunmawar da ya ke baiwa jam’iyyar APC a jihar Kano da kuma Arewacin Najeriya.

Shettima ya ce tabbas jam’iyyar na alfahari da matasa irinsu Ja’o’iji wadanda ke aiki tukuru dan bunkasa jam’iyyar.

Haka zalika Shettima ya ce jam’iyyar na sane da irin kabakin alkairi da Ja’o’ji ke yiwa matasa da mata a jihar Kano.

Kwamishina a Kano ya mayar da rarar Naira Miliyan 100 Asusun Gwamnati

A lokacin da ya ke bayani, Ja’oji ya godewa mataimakin shugaban kasar kan tarbar da ya yi masa.

Ya kuma yi alkawarin ninka gudunmawar da ya ke bawa jam’iyyar ta hanyar bada tallafi ga matasa da mata kamar yadda ya saba.

A watan Disamba shekarar da ta gabata Ja’o’ji ya bawa matasa da mata tallafin miliyan 500 don su dogara da kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...