Kwamishina a Kano ya mayar da rarar Naira Miliyan 100 Asusun Gwamnati

Date:

 

Sabon Kwamishinan Ƙananan Hukumomi na jihar Kano, Alhaji Tajuddin Usman ya mayar da Naira miliyan 100 ga asusun gwamnatin jihar.

Usman ya mayar da kuɗin ne na rarar kuɗaɗen kwangilar dinka tufafin makaranta ga ɗaliban firamare dubu 789 a fadin ƙananan hukumomi 44 na jihar.

Talla

Kwamishinan, wanda shi ne shugaban kwamitin raba kayan, ya mayar da rarar kudaden da aka ware domin ɗinkawa daliban firamare sabbin tufafin makaranta, inda kuɗaɗen su ka yi ragowa bayan da aka kammala aiki kuma shugaban kwamatin ya kuma dawo dasu.

Rahma Radio ta rawaito cewa Usman ya bayyana hakan yayin kaddamar da rabon kayan a gidan gwamnatin Kano a jiya Litinin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...