Dubun wani matashi da ya sace yaro dan shekaru 2 ta cike a Kano

Date:

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, sun kama wani matashi mai shekaru 25, kan zargin sace wani yaro ɗan shekara biyu a duniya, Al’amin Ahmad Garba, tare da neman kuɗin fansa Naira miliyan 50.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar 25 ga watan Disamban 2024.

Talla

An gano yaron a wani gida da ke unguwar Dorayi bayan ya shafe kwanaki uku a ɓoye.

Bayan an ceto yaron, an kai shi Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad don duba lafiyarsa, sannan aka miƙa shi ga iyayensa.

Dalilin da yasa za a fuskanci katsewar wutar lantarki na akalla sati biyu a Abuja

An gurfanar da wanda ake zargin a kotun majistare mai lamba 25 da ke Nomansland, a Kano.

Kakakin ya ce matashin yanzu haka yana tsare a hannun hukuma, yayin da ake ci gaba da shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...