Dubun wani matashi da ya sace yaro dan shekaru 2 ta cike a Kano

Date:

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, sun kama wani matashi mai shekaru 25, kan zargin sace wani yaro ɗan shekara biyu a duniya, Al’amin Ahmad Garba, tare da neman kuɗin fansa Naira miliyan 50.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar 25 ga watan Disamban 2024.

Talla

An gano yaron a wani gida da ke unguwar Dorayi bayan ya shafe kwanaki uku a ɓoye.

Bayan an ceto yaron, an kai shi Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad don duba lafiyarsa, sannan aka miƙa shi ga iyayensa.

Dalilin da yasa za a fuskanci katsewar wutar lantarki na akalla sati biyu a Abuja

An gurfanar da wanda ake zargin a kotun majistare mai lamba 25 da ke Nomansland, a Kano.

Kakakin ya ce matashin yanzu haka yana tsare a hannun hukuma, yayin da ake ci gaba da shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...