Shugaban karamar hukuma a Kano ya kwace wata makarantar Islamiyya saboda ta gayyaci Sarkin Aminu Ado Bayero

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Shugaban karamar hukumar Nasarawa Amb. Imam Yusuf ya Kwace wata makarantar Islamiyya saboda ta sanya hoton Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a cikin kalandar makarantar tare da gayyatar Sarkin.

” Ba za mu lamunci wata makaranta ta sanya hoton wani wanda ba Sarki ba a cikin kalandar, saboda yin hakan neman kawo cikas ne ga zaman lafiyar da muke da shi a Nasarawa”.

Kadaura24 ta rawaito cewa Amb. Imam Yusuf ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai a Ofishinsa.

Talla

” A kawai wata makarantar Islamiyya mai suna Ubaiyu Bn Ka’ab dake unguwar gama a karamar hukumar Nasarawa da ta dauki hoton wani wanda ba shi bane sarki Kano a cikin kalandarta tare kuma da gayyatarsa wannan abun da suka yi ya saba dokarmu”. Inji ogan Boye

Shugaban karamar hukumar Nasarawa ya ce su a saninsu khalifa Muhd Sanusi II shi ne Sarkin Kano, don haka ba za su lamunci wani ko wata su rika kiran wani Sarkin Kano ba , alhakin kuma ba shi ba ne.

Majalisar Shura ta Darikar Tijjaniyya ta yabawa Gwamnan Kano bisa Nadin Habib Dan almajiri

Ya ce ya Kwace makarantar daga wannan rana ya mayar da makarantar karkashin kulawar Sakataren ilimi na karamar hukumar tare da rushe duk shugabannin makarantar.

” Daga yau Ina ba da umarnin kada wata makaranta ko hukuma ta gwamanti ko mai zaman kanta ta sake sanya hoton wani Sarki wanda ba Sarki Sanusi na II ba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...