Shugaban karamar hukuma a Kano ya kwace wata makarantar Islamiyya saboda ta gayyaci Sarkin Aminu Ado Bayero

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Shugaban karamar hukumar Nasarawa Amb. Imam Yusuf ya Kwace wata makarantar Islamiyya saboda ta sanya hoton Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a cikin kalandar makarantar tare da gayyatar Sarkin.

” Ba za mu lamunci wata makaranta ta sanya hoton wani wanda ba Sarki ba a cikin kalandar, saboda yin hakan neman kawo cikas ne ga zaman lafiyar da muke da shi a Nasarawa”.

Kadaura24 ta rawaito cewa Amb. Imam Yusuf ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai a Ofishinsa.

Talla

” A kawai wata makarantar Islamiyya mai suna Ubaiyu Bn Ka’ab dake unguwar gama a karamar hukumar Nasarawa da ta dauki hoton wani wanda ba shi bane sarki Kano a cikin kalandarta tare kuma da gayyatarsa wannan abun da suka yi ya saba dokarmu”. Inji ogan Boye

Shugaban karamar hukumar Nasarawa ya ce su a saninsu khalifa Muhd Sanusi II shi ne Sarkin Kano, don haka ba za su lamunci wani ko wata su rika kiran wani Sarkin Kano ba , alhakin kuma ba shi ba ne.

Majalisar Shura ta Darikar Tijjaniyya ta yabawa Gwamnan Kano bisa Nadin Habib Dan almajiri

Ya ce ya Kwace makarantar daga wannan rana ya mayar da makarantar karkashin kulawar Sakataren ilimi na karamar hukumar tare da rushe duk shugabannin makarantar.

” Daga yau Ina ba da umarnin kada wata makaranta ko hukuma ta gwamanti ko mai zaman kanta ta sake sanya hoton wani Sarki wanda ba Sarki Sanusi na II ba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...