Babu wanda ya sauke Sarkin Sanusi II daga khalifancin Tijjaniyya a Nigeriya – Sheikh Sani Auwalu

Date:

Khalifan Tijjaniyya na duniya Sheikh Ibrahim Mahy Inyass ya musanta batun sauke Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II daga khalifancin Tijjaniyya na Nigeria.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa guda cikin masu magana da yawun Khalifa Sheikh Mahy wato Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi ya bayyanawa kadaura24 cewa an sauke sarkin Sanusi II daga khalifancin Tijjaniyya saboda ya dawo gadon sarautar Kano.

Talla

A wata ganawa da Manema labarai a Kano guda cikin masu magana da yawun Khalifa Sheikh Mahy wato Sheikh Sani Auwalu Ahmad ya ce batun da Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi ya yi na sauke sarki Sanusi II ba shi da tushe ballantana makama.

Dalilin da yasa aka sauke Sarki Sanusi II daga Khalifancin Tijjaniyya a Najeriya – Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi

” Jawabin da Alhaji Ibrahim Dahiru Bauchi ya yi ba shi da wata madogara, duk da shi ma yana daga cikin masu magana da yawun Shehi Mahy, maganar ba gaskiya ba ce kawai yana son ya hada husuma ne, da kuma kokarin nemawa kansa suna”.

Ya bukaci al’ummar Nigeriya da duk mabiya darikar Tijjaniyya da su yi watsi da waccen maganar ta sa, domin ba ta da wani tushe kuma ba da yawun Shehi Mahy ya yi ta ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...