Dalilin da yasa aka sauke Sarki Sanusi II daga Khalifancin Tijjaniyya a Najeriya – Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Rahotanni na cewa Shugaban ƙungiyar Tijjaniyya na Afrika, Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Inyass, ya sanar da tsige Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II daga matsayin Khalifan Tijjaniyya a Najeriya.

Wannan sanarwa na ƙunshe ne cikin wata takarda wacce aka rubuta kuma aka aikewa manema labarai da sauran mambobin darikar Tijjaniyya da ke faɗin Najeriya a ranar Talata 26th ga watan Nuwambar, 2024.

Takardar mai ɗauke da sa hannu da Stampin shugaban ƙungiyar Tijjaniyya na Afrika, Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Inyass, ta ce daga yau ta Cire Muhammadu Sanusi II daga Khalifancin Tijjaniyya kuma ta soke ofishin Khalifancin Tijjaniyya a Najeriya.

Talla

Da yake yiwa Kadaura24 karin bayani mai magana da yawun Sheikh Mahy Sheikh Ibrahim Inyass wato Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi yace Sheikh Dahiru Usman Bauchi da Sheikh Shariff Ibrahim Saleh Al-Husain ne za su cigaba da gudanar da duk wasu harkokin darikar Tijjaniyya dake faɗin Najeriya .

“Da ma a darikar Tijjaniyya ba a baiwa sarki khalifanci, ko a baya ma an baiwa Sarki Sanusi na 1 khalifancin Tijjaniyya ne bayan da aka sauke shi daga sarkin Kano, haka shi ma Muhammadu Sanusi II sai da aka sauke shi sanann aka ba shi, saboda kar ya shiga damuwa”. Inji Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi

Madakin Gini ya yiwa Kwankwaso martani kan batun tsige shi daga muƙaminsa na majalisa

“Tun a baya Sheikh Mahy Inyass ya so ya karbe khalifancin na Muhammadu Sanusi II, amma sai aka ba shi shawarar idan aka sauke shi zai ji cewa an wulakanta shi, shi yasa aka bar shi, amma yanzu tunda ya ce ya dawo sarautar Kano to shi yasa aka cire shi tunda ya zabi Sarauta fiye da khalifancin Tijjaniyya”.

Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi ya bukaci dukkanin yan darikar Tijjaniyya da su Kasance masu biyayya ga wannan umarni domin samar da masalaha a darikar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...