Rikicin NNPP: Gwamnan Kano ya Bijirewa Umarnin Kwankwaso, na cire wasu jami’an gwamnati

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Gwamnan jihar Kano Abba Yusuf ya ki bin umarnin uban gidan sa Sanata Rabi’u Kwankwaso na cire wasu manyan jami’an gwamnati, lamarin da ya haifar da fargabar barkewar rikici.

Mutanen da Kwankwaso ke son a tsige su, kamar yadda NAN ta ruwaito, sun hada da Kwamishinan Yada Labarai, Baba Dantiye, da Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Dr Abdullahi Bichi.

Talla

Wata majiya ta shaida wa kamfanin dillacin labarai NAN a ranar Talata cewa Kwankwaso bai ji dadin zargin Bichi na kin karbar umarni daga wajensa ba wajen gudanar da wasu ayyukansa .

NAN ta tattaro cewa jagoran jam’iyyar NNPP na kasa yana son a maye gurbin Dantiye da wani dan soshiya midiya wanda yake ganin ya fi cancantar tafiyar da ma’aikatar da kuma kare martabar gwamnatin jihar.

Sanata Kawu Sumaila ya zargi yan majalisa da daukar nauyin shaye-shayen matasa

Majiyoyin da ke kusa da gwamnan sun ce gwamna Yusuf ya gwammace ya tattauna da Kwankwaso kan lamarin maimakon ya yi aiki da ‘umarnin nasa.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito ce wata kungiya ta bulla a Kano mai suna “Abba Tsaya Da Kafarka” Mai rajin Abba ya ya bijirewa uban gidansa”.

Talla

Rahotanni sun nuna cewa kungiyar ta yi imanin cewa Kwankwaso ne ya zabo mafi yawan masu rike da mukaman siyasa na gwamnati da suka hada da kwamishinonin da dai sauransu .

Binciken NAN ya kuma gano cewa ‘yan majalisar tarayya na jam’iyyar NNPP kwanan nan sun gana da Yusuf inda suka bukace shi da ya tabbatar da ‘yancin kan sa.

Talla

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban NNPP na jihar Kano Hamisu Dumgurawa ya sanar da dakatar da sakataren gwamnatin jihar kano Baffa Bichi da kuma kwamishinan sufuri Muhammad Doggon daga jam’iyyar.

Ya ce an dakatar da su ne bisa zargin cin zarafin jam’iyya.

Da NAN ta tuntubi Kwankwaso ya ki cewa komai game da lamarin, sai ya ce: “Ba zan ce komai akan wannan batun ba tunda shugaban jam’iyyar ya riga ya dauki matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...