Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Zakari Sarina, ya zama kwamishinan hukumar korafe-korafen jama’a ta kasa (PCC), mai wakiltar jihar Kano.

Sarina ya maye gurbin Hon Yusuf Abdullahi Ata, wanda aka nada shi a matsayin karamin ministan gidaje da raya birane.

 

Ata ya kasance kwamishinan PCC mai wakiltar jihar Kano daga Yuli zuwa Oktoba 2024 kafin shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya nada shi a matsayin minista.

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Obot Akpabio, ne ya sanar da nadin Sarina a zaman na yau.

Sarina, dai yanzu haka shi ne sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare...

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

  Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar...

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...