Abun da Baffa Babba ya yiwa matasan Kano zai kara musu kwarin gwiwa – Sharu Sani Madigawa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Wani malami a Kano mai suna sharu sani Madigawa ya yabawa Shugaban hukumar ingantuwar aiyukan ta kasa Baffa Babba Dan’agundi Bisa yadda ya dauki yan jihar kano ya basu mukamai daban-daban a Ofishinsa.

” Ina yabawa Baffa Babba Dan’agundi saboda ya yi abun da ya dace na baiwa Matasa mukamai , saboda irin gudunmawar da suka bayar yayin zaɓen da ya gabata, hakan zai karawa matasa kwarin gwiwar shiga Siyasa”.

Talla

Sharu Madigawa ya bayyana hakan ne yayin da ya gana da wakilin jaridar kadaura24.

Rikicin NNPP: Gwamnan Kano ya Bijirewa Umarnin Kwankwaso, na cire wasu jami’an gwamnati

‘ Ina mafani da wannan dama wajen taya Nabila Bature murna Bisa mukamin da Baffan ya bata na wakiliyarsa a Kano ta yadda zata rika sanya idanu akan duk abun da ya shifi yan kungiyoyin Support Group”. Inji sharu madigawa

Talla

Ya ce yana da yakinin Nabila Bature zata yi aikin ta yadda ya dace domin ciyar da jam’iyyar APC gaba a jihar kano, da kuma kyautata alaka tsakanin Baffa Babba Dan’agundi da yan kungiyoyin Support Group.

Talla

Ya bukace ta da ta zama mai gaskiya da rikon Amana, Sannan ta yi aiki tukuru domin sauke nauyin da Baffa Babba Dan’agundi ya dora mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...