Gwamnan Kano ya nada sabbin Sarakuna 3 masu daraja ta biyu

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin sabbin sarakunan da zasu jagoranci masarautun Rano, Gaya da Kuma karaye a matsayin sarakuna masu daraja ta biyu.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Talla

Sarakunan da aka nada sun hadar da Alhaji Muhammad Mahraz Karaye a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin nadin nasa shi ne hakimin karamar hukumar Rogo.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya sanya hannu a sabuwar dokar karin masarautu

Sai Alhaji Muhammad Isa Umar a matsayin Sarkin Rano wanda kafin nadin nasa shi ne hakimin karamar hukumar Bunkure.

Sai kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya a matsayin Sarkin Gaya wanda a baya shi ne tsohon Sarkin masarautar Gaya wadda aka rushe.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hori sabbin sarakunan masu daraja ta biyu da su zamo masu hada kan al’umarsu da tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa al’adu a masarautunsu daban daban.

Sanarwar tace nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...