Gwamnan Kano ya nada sabbin Sarakuna 3 masu daraja ta biyu

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin sabbin sarakunan da zasu jagoranci masarautun Rano, Gaya da Kuma karaye a matsayin sarakuna masu daraja ta biyu.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa kadaura24.

Talla

Sarakunan da aka nada sun hadar da Alhaji Muhammad Mahraz Karaye a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin nadin nasa shi ne hakimin karamar hukumar Rogo.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya sanya hannu a sabuwar dokar karin masarautu

Sai Alhaji Muhammad Isa Umar a matsayin Sarkin Rano wanda kafin nadin nasa shi ne hakimin karamar hukumar Bunkure.

Sai kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya a matsayin Sarkin Gaya wanda a baya shi ne tsohon Sarkin masarautar Gaya wadda aka rushe.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hori sabbin sarakunan masu daraja ta biyu da su zamo masu hada kan al’umarsu da tabbatar da zaman lafiya da kuma bunkasa al’adu a masarautunsu daban daban.

Sanarwar tace nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...