Ya kamata Gwamnatin Kano ta Mutunta Umarnin Kotu – Dr. JY

Date:

Daga Rahama Usman

 

Tsohon kwamishinan harkokin noma na jihar kano Dr. Yusuf Jibril JY ya bukaci gwamnatin jihar da ta bi umarnin kotun tarayya na tabbatar da dawo da Sarakunan Rano Gaya Bichi da Karaye.

” Muna da kyakykyawan yakinin gwamnatin za ta mutunta umarnin kotu saboda ta amfani hukuncin kotu don haka ita yafi dacewa ta mutunta umarnin don kiyaye doka da Oda”.

Yanzu-yanzu: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Sarautar Kano

Dr. Yusuf Jibril JY ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da jaridar kadaura24, jim kadan bayan hukuncin kotu.

Ya ce mutunta umarnin kotun zai kara fito da kimar gwamnatin, amma rashin bin umarnin kuma zai zubar da kimar gwamnatin a idon al’ummar jihar kano da kasa baki daya .

Hadimin gwamnatin Kano ya yiwa Kawu Sumaila, Hanga da yan majalisu 17 wankin Babban Bargo kan rikicin Sarauta Kano

Dr. JY ya bukaci al’ummar jihar Kano da su gudanar da murnar dawo da Sarakunan su cikin kwanciyar hankali da lumana, ba tare da karya doka ba.

” Ina amfani da wannan dama wajen taya mai martaba Sarki Rano Alhaji Dr. Kabir Muhammad Inuwa, bisa dawo da shi kan karagarsa ta Sarautar Rano wadda aka ba cire shi ba bisa ka’ida ba”. A cewar Dr. JY

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya...

Aiyuka 5 da Gwamnan Kano ya yi alkawarin yi, bayan dakatar da rusau a Rimin Zakara

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci garin Rimin Zakara...

Shugaban K/H Garun Mallam zai Raba Audugar Mata 500 ga Makarantun Sakandiren Matan yankin

Daga Safiyanu Dantala Jobawa Shugaban karamar hukumar garun mallam Aminu...

Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...